|
|
| |||
|
Addinin Musulunci
v
Musulunci
shi ne addini mafifici kuma shi ne mafi tsarki a cikin dukkan addinan duniya.
v
Musulunci
ya zo ne domin ‘yan Adam, ba Musulmai ko Iraniyawa kadai ba. An aiko Annabawa
ga mutane ne, haka Annabin Musulunci an aiko shi ga dukkan mutane ne.
v
Musulunci
ya zo domin gyara bil Adama ne.
v
Musulunci
addinin gyaran mutum ne.
v
Abin
da Musulunci ya damu da shi shi ne ginawa da tarbiyantar da mutum domin kuwa
don hakan ya zo.
v
Musulunci
yana fada da duk wani abin da zai mai da mutum maras amfani kuma abin kyama.
v
Musulunci
addini ne da aka saukar don ya karfafa ko gina ‘yan’Adam.
v
Don
haka, Musulunci mafita ce ga dukkan wani al’amari na duniyan nan da ma daya
duniyar.
v
Tare
da irin wannan makaranta ingantacciya kamar Musulunci, babu wani dalili da zai
sa Iraniyawa za su koyi nau’in rayuwar yammaci ko gurguzu ba.
v
Idan
aka musuluntar da komai, za a samu tsarkakakkiyar
al’umma.
v
Musulunci
domin gyaran al’umma yake.
v
Dokokin
Musulunci ingatattu, cikkakku da masu taimakawa ne.
v
Musulunci
na ba da karfi a
v
Musulunci
na a mataki na koli a ci gaba, haka kuma masanansa na addini.
v
Musulunci
ya yarda da dukkan abubuwan ci gaba na zamani sai dai wadanda ke gurbata dabi’u
da bata kyawawan ayyuka. Musulunci ya yi watsi da abubuwan da ke sabawa
maslahar al’umma, amma kuma yana karfafa abubuwan da ke dacewa da dukkan
bukatun al’umma.
v
Abubuwan
da Musulunci ke inkarinsu su ne wadanda ke janyo matasammu zuwa fasadi.
v
Doka
daya ce, Musulunci, ta hukumcin Allah kawai.
v
Muna
imanin cewa akidar da ke iya shiryarwa da sa ci gaban al’umma ita ce kawai
Musulunci. Kuma idan duniya na son fitowa daga duhun matsalolin da take ciki a
yau, da kuma samun rayuwa ta ‘yan adamtaka, to wajibi ta shiga sahu guda da
Musulunci.
v
Musulunci
ya zo ne domin ceton dan adam.
v
Musulunci
ya zo ne domin ci gaba, kuma musulunci na da ra’ayi mai kyau game da ci gaba.
v
Zaman
Musulunci a abu shamili da kuma zama gama gari, zai sa duk wanda ya fahimce shi
ya yarda da cewa: Musulunci ya wuce haddin tunanin mutum kuma ba zai iya zamowa
abin da karfin kimiya ko kwakwalwar (ko basirar) mutum ke iya kirkirowa ba.
v
Musulunci
ba mallakar wata kasa ce ba, bai san Baturke ko Bafarishe (Bairaniye) ko
Balarabe ba ko Ba’ajame ba, Musulunci na kowa ne, abubuwa kuma irin su zuri’a,
launin fata, kabila ko yare ba su da matsayi.
v
A
Musulunci al’amarin tushe ko zuri’a ba
abin zance ne ba, Larabawa ko wadanda ba Larabawa ba da sauran kabilu ba
abin tattaunawa bane a Musulunci.
Musulunci ya zo ne domin gina mutum da ilmintar da shi. Muhimmin abu a
Musulunci shi ne tarbiyantar da mutum da kuma gina shi.
v
Musulunci
ya zo ya hada kan dukkan al’ummomin duniya, Balarabe, Ba’ajame, Baturke ko
Bafarishe dukkansu zuwa ga ginin babbar
al’umma daya, wato, al’ummar Musulunci, domin cewa wadanda ke neman danne
kasashen musulmi da cibiyoyin Musulunci sun kasa yin haka ne sabili da kasaicin
al’ummar da Musulunci ya gina wadda ta kumshi kabiloli daban-daban.
v
Abin
da ya hado dukkan kungiyoyin kabiloli daban-daban a karkashin runfa guda shi ne
kudurar Musulunci.
v
Na
sha fadin cewa zuri’a, harshe,kasanci, ko mazauni a bayan kasa ba muhimman
abubuwa ba ne a Musulunci.
v
Dokar
Musulunci ba ta ha’inci a tsakanin mutane.
v
Musulunci
akidar mutanen da ke a tafarkin neman gaskiya da adalci ne; akidar wadanda ke
neman ‘yanci da mulkin kai ne; kuma akidar masu fada da ‘yan mulkin mallaka ne.
v
Wajibi
ne mu yi kokarin rusa bangunan jahilci da camfe-camfe ta yadda za mu sami daman
isa ga wannan tsarkakakken addini na Annabi Muhammadu (s.a.w.a.).
v
Hakika
shaidanu suna kokarin su rusa wannan addini na Musulunci.
v
A
yau, Musulunci yana kalubalantar duk wani nau’i na kafirci.
v
Lalle,
a halin yanzu babu wani karfi da zai iya fuskantar Musulunci.
v
Ku
rike Musulunci a matsayin shugabanku kuma mai shiryar da ku sannan ku mika masa
wuya.
v
Musulunci
ya fi zama abin kauna bisa ga yadda muke tsammani.
v
Makarantar
Musulunci, makaranta ce ta tsarkakarwa da gogewa.
v
Musulunci
na daidaitar da abubuwan duniya ta hanyar da za su hadu da na lahira (addini).
v
Musulunci
ya fadi komai, amma mai wuyan ya saura ga Musulmai.
v
Babbar
matsalar Musulmai, ita ce rabuwarsu da Musulunci da Alkur’ani.
v
Idan
al’ummomi za su fahimci Musulunci, to za su san cewa duk abin da suke nema suna
iya samunsa a Musulunci.
v
Duk
cutarwa da wannan duniya ta fuskanta an same shi sakamakon rashin fahimtar
Musulunci daga wasu mutane.
v
Masu
mummunar ra’ayi na Musulunci su ne wadanda ba su fahimci Musulunci ba.
v
Ina
kira gare ku da kada ku juya wa Musulunci baya, kada ku juya wa malamai baya,
domin wadannan wasu falaloli ne na Ubangiji, kada ku
v
Hakika
martabar Musulunci da malamai yana fuskantar barazana daga ‘yan waje.
v
Musulunci
yana umurtan gwamnatoci da su zama masu hidima (ga mutane).
v
Musulunci
ya kasance mai hidima ga marasa galihu.
v
Musulunci
zai tabbatar da farin ciki da jin dadinku a nan duniya da kuma lahira.
v
Hakika
Musulunci ya kawo mana komai.
v
Musulunci
ya zo ne don ya ceto raunana.
v
Musulunci
shi ne addinin ‘yanci da walawa.
v
Musulunci
ya yarda da neman abin duniya don kare mutumci.
v
Musulunci
na samar da kwanciyar hankali kuma yana kiyaye hanyoyin cimma buri.
v
Dokokin
Musulunci sun yi daidai da bukatun dan Adam kuma wadannan dokoki a fili suke.
v
A
dukkan janibobi na siyasa, tattalin arziki, al’adu da taimakekkeniya, Musulunci
yana da hanyar hakikanin ci gaban dan Adam.
v
Makarantar
Musulunci ba ta allaku da madda ba, ita makaranta ce ta dabi’u masu kyau wadda
ta yarda da abubuwan madda a karkashin Ahalak, dabi’u na gari da tsarkake
zuciya.
v
Musulunci
bai zama na ginin dabi’u masu kyau kawai ba, ko na abubuwan madda kawai ba, ya
hada duka. Shi ne cewa, Musulunci da Alkur’ani mai girma sun zo ne domin
bunkasa da gina mutum a dukkan nau’oin rayuwarsa.
v
Musulunci
mulkin Uluhiya ne nau’i daya shine na siyasa, nau’i dayan kuwa na ginin
dabi’u masu kyau ne.
v
Musulunci
akida ne na ibada da siyasa; sannan ibada ko bauta suna cikin al’amurran siyasa
da kuma nau’oinsa na ibada ya kunshi siyasa.
v
Manzon
Allah (s.a.w.a.) ya assasa ginshikin siyasa a addini. Kuma Manzon Allah
(s.a.w.a.) ya assasar da hukumcin gwamnati.
v
Dokoki
da fatawoyin siyasa na Musulunci sun fi na ibada yawa.
v
Nishadin
siyasa wajibi ne na addini a Musulunci.
v
Da
rantsuwa da Allah, Musulunci, a dukkansa siyasa ce.
v
Kiyaye
hakkin mutane ra’ayi ne na Musulunci.
v
Addinin
Musulunci siyasa ce ta kowace hanya, har a cikin ibada.
v
Musulunci
yana da shirye-shirye a
v
Musulunci
ya tsara hanyoyin wa dukkan rayuwar
mutum daga lokacin haihuwarsa zuwa shigarsa cikin kabari.
v
Al’amurran
zamantakewa da siyasa na mutum anfi ba su alfarma bisa ga na ibada a wurin lura
da dokokin Musulunci.
v
Musulunci
na da tsari na rayuwa da tsari na gwamnati.
v
Dokokin
Musulunci suna sa ci gaba na koli, da tabbatar da ‘yanci, mulkin kai da bunkasa.
v
Kasar
da ke aiwatar da dokokin Musulunc, da gaskiya, za ta zama kasa mafi ci gaba.
v
Shi
kansa Musulunci, ya kasance daya daga cikin wadanda suka kawo ko kafa manyan
hanyoyin ci gaba da kuma wayewa a duniya.
v
Musulunci
da fadin Allahu Akbar ne suka kai ku ga cin nasara.
v
Musulunci
ne ya iza ku kuma ya ba ku irin wannan karfi har kuka yi tsayuwar daka a gaban
karfafan rundunonin Shaidan ba ku tsorata ba.
v
Ba
da ‘yancin zartarwa ga wadanda ke da nufin yi wa Musulunci da jama’a makirci,
ha’inci ne.
|
||||