Annabawan Allah

v    Annabawa sun zo ne domin sanya kudurorin da aka tanada zuwa na aiwatarwa da kuma su kai dan’Adam zuwa ga ainihin dan’Adam na gaskiya.

v    Dukkan kokarin Annabawa ya kadaita ne wajen kiran dan’Adam zuwa ga hanya madaidaiciya (gaskiya) da sa shi ya bi tafarkinta.

v    An aiko Annabawa ne  domin su kubutar da halayen mutane da zukatansu da ruhinsu daga dukkan duhu sannan su maye gurbinsu da haske.

v    Annabawa sun zo ne domin kiran mutane daga duhu zuwa ga haske.

v    Sakon Annabawa ya kawo canje-canje na kimiya da irfani, sanin Allah a duniya ya sauya sandararriyar falsafar kasar Girka (Greek) wadda su kansu Girkawa suka kago wadda ta kasance mai muhimmanci har yanzu zuwa wata fahimta ta ilimin irfani da kai wa ga hakika ta gaskiya irin ta manyan masana hakika.

v    Abin da Annabawa suke bukata shi ne sauya dukkan al’amura na rayuwa da na halitta da kuma mutum su dace da yardar Allah.

v    Albarkar aiko Mafificin Annabawa albarka ce da tun da, kama daga farkon halitta zuwa karshen lokaci, ba a samu ba kuma ba za a taba samun irin ta ba.

v    “Zillullah” (wato inuwar Allah) shi ne Shugaban Manzanni wanda shi a kan kansa babu wani abu daga gare shi, duk komai wahayi ne.

v    Tsira da amincin Allah Mai girma su tabbata ga Annabi Isa dan Maryama (a.s), Ruhullah Manzon Allah Mai girma wanda ya kasance yana tayar da matattu. Tsira da amincin Allah su tabbata ga mahaifiyarsa tsarkakakkiya Maryama, wacce, ta hanyar hura ruhin Allah, ta haifi wannan irin da mai albarka ga wadanda ke jin kishirwar rahamar Allah.

v    (Jawabi ga limaman Kirista) Domin samun yardar Allah da aikata abin da Isa (a.s) ya umurta, ku kada kararrawar cocin ku domin kare Iraniyawa raunana da kuma yin tir da zaluncin  azzalumai.

v    Ainihin aikin Annabawa shi ne magance son rai gwargwadon iko kuma su shiryar da zuciya.

v    Mu masu neman abu mafi alheri ga al’umma ne; mu mabiya Annabawa ne wadanda sun zo domin gyaran al’umma, sun zo ne domin ja-gorancin al’umma zuwa ga sa’ada.

v    Idan da dukkan Anabawa za su hadu wuri guda, ba za su taba sabawa da juna ba.

v    Idan dukkan Annabawa (a.s) za su zo a lokaci guda, ba za su taba samun sabani da juna ba.

v    Annabawa basu daukar takobi wa kowa sai kawai a kan wadanda takobin shi ne magani a gare su, wadanda suke kawo fasadi a cikin al’umma.

v    Hikimar Annabawa ita ce gallaza wa kafirai da makiya bil adama, da kuma rausasawa ga junansu, wannan gallazawar ita kanta rahama ce.

v    Annabawa sun kasance suna jin tausayin kafirai da munafukai da yin mamakin yadda suka zama yadda suke.

v    A farkon kiransu, Annabawa sun fuskanci masu hannu da shunin al’umma ne, Annabi Musa (a.s) ya fuskanci Fir’auna. Masu galihu su ne suka fi cancantar a fuskance su don su shiryu.