|
|
| |||
|
Gyara Kai Da Fada Da Son Zuciya
v
Ba
za mu iya gyaran kasarmu ba, matukar ba mu fara da gyaran kanmu ba.
v
Dole
ne kowa ya fara da kansa, aikinsa da akidarsa da kuma dabi’unsa, ya yi su
daidai da dokokin Musulunci, sannan bayan haka sai ya dauri aniyar gyaran
wadansu.
v
Idan
kuna son kasarku ta zama mai hakikanin mulkin kai, ta yadda wasu ba za su iya
katsalandan a cikinta ba, to ku fara da kanku.
v
Ku
gyara kanku, kasarku ita ma za ta gyaru.
v
Abin
da ke da muhimmanci ga kowannenmu shi ne fara yaki da zuciya da bin son ranmu
da kuma kin gamsuwa da cewa da wannan gyaran zahirin komai zai yi daidai, dole
ne mu fara da zukatanmu da kwakwalenmu, kuma kullum mu yi kokari mu ga cewa
ranarmu ta biyu ta fi ranar da ta gabata.
v
Ilimin
kyautata dabi’u na Musulunci kamar su gyaran hali da tsarkake zuciya da shiga
tafarkin kusanci ga Allah na daga muhimman fannonin ilimi na yaki da zuciya
wadanda suka zamanto wajibi a
v
Ilimi
da tsarkake zuciya ne suke sa mutum ya kai ga matsayin ‘yan Adamtaka.
v
Mantawa
da amfanin kai ita ce share fagen kaiwa ga kamalar ‘yan Adamtak.
v
Mu
yi nazarin ayyukanmu na duniya kafin a gabatar da su ga Imamuz Zaman (a.s)
sa’an nan a isar da su ga Allah Madaukakin Sarki.
v
Ku
yi aikin da in kuka dauke guzurinku daga nan za ku tashi da farar fuska a gaban
Allah.
v
v
Wajibi
ne ku gyara kanku ta hanyar da za ku iya yunkurowa domin gyaran kai da nufin
biyayya wa umurnin Allah.
v
Idan
muka gyara kanmu, tabbatacce ne cewa, manufarmu ita ma za ta yadu a duniya.
v
Gyaran
ruhi da tsarkake shi yana
v
Ku
ginu! Wajibi ne mu gina kanmu! Ku yi kokarin fara jihadin ginin kai ta hanyar
farawa da kanku, zai zamanto dukkan abin da ku ke yi, na Ubangiji ne.
v
Wajibi
ne mu samu juyin juya hali a zukatanmu, ruhinmu ya canja dole ne ya sami juyin
juya hali. Wajibi ne mu canza idan ya zuwa yanzu ruhinmu ya kasance a karkashin
Shaidan da dagutu, to lalle ne mu canza.
v
A
ruhin da ba a tsarkake ba, ilimi zai zama shingen duhu.
v
Wajibi
ne na addini cewa idan a cikinmu ba ma jituwa da wasu, to a maganganunmu da
ayyukanmu da wa’azinmu mu zama mun sabawa wa son ranmu a aikace.
v
Idan
ba a tsarkake zuciya ba to ilimi ya fi jahilci cutarwa.
v
Magana
ta fi ratsa zuciya da tasiri ne idan ta fito daga tsarkakakkiyar zuciya.
v
Idan
mutum ya iya ya take “Ni” a karkashin kafarsa ya canza ta zuwa “Shi”, to zai
iya gyara dukkan abubuwa su zama daidai.
v
A
wani lokaci ilimin tauhudi na kai mutum wuta, kuma wani lokaci ilimin irfani ma
ya
v
Ilimin
Tauhidi, shi ma idan ya ta’allaka da wanin Allah ne to yana daga shamakin duhu.
v
Allah
Ya kiyaye, mutum ya shiga cikin al’umma kuma ya samu girma da karbuwa a cikin
jama’a, kafin ya tsarkake zuciya daga bin son rai, domin babu shakka zai yi
hasara ya halaka kansa.
v
Duk
wanda ya dogara ga Allah zai ci nasara.
v
Idan
kuka fita faga wannan duniya, wadda ita ce fagen ginin rayuwar lafiya, kun
makara kuma ba za ku iya tsarkake rayukanku daga fasadi ba.
v
Ina
tsoron cewa kada ta hanyar sauraren kalamominmu kuma saboda mu, su shiga aljanna
mu kuma mu shiga wuta domin ba mu tsarkake kanmu ba.
v
Bukin
idi na hakika shi ne lokacin da mutum ya samu yardar Allah, ya gyara kansa da
zuciyarsa.
v Jama’ar
kasa, ko wata al’umma ba za ta iya cimma manufofinta ba har sai ta tsarkake da
kuma gyara kanta.
|
||||