Shahada Da Shahidai

v    Shahada daukaka ce madawwamiya.

v    Shahada abin alfaharin waliyai ce, mu ma abin alfaharinmu ce.

v    Tsoro na ga wanda akidarsa ba shahada ce ba.

v    Shahada sirrin nasara ce.

v    Al’ummar da ke fatan shahada ta ci nasara.

v    Ku idan kuka yi galaba a duniya kunci nasara haka idan kuka yi shahada duk dai ku ne masu nasara.

v    Shahada a tafarkin Musulunci abin alfahari ne gare mu dukanmu.

v    Shahada albarka ce mai girma gare mu.

v    Wannan irin jin neman da kuma zama a shirye domin sadaukar da kai shi ne ya sa al’umma hannu rabbana ta yi galaba a kan dagutu.

v    Al’ummar da matanta da mazajenta a shirye suke da su bayar da     rayukansu kuma suna neman shahada, babu wani karfi da zai iya kalubalantarta.

v    Jinin shahidanmu ci gaba ne na tsarkakekken jinin shahidan Karbala.

v    Al’ummar da shahada abin daukaka ne gare ta, to taci nasara.

v    Al’ummar da ke son yin shahada ba ta  da wani jin tsoro.

v    Jama’ar al’umarmu ta bayar da jini domin a samu Jamhuriyar Musulunci .

v    Jama’ar al’ummarmu sun kasance masu burin shahada ne, kuma da burin shahadan ne wannan yunkurin ya tabbata da ya kuma ci gaba.

v    Daga Allah mu ke dukanmu, dukkan halittu daga Allah suke baki daya, alamun samuwar Allah ne, kuma komai zai koma zuwa gare Shi ne. Don haka abin da ya fi komawar ta zama ta hanyar  zabin da zabar wa kai, mutum ya zabi shahada a tafarkin Allah, kuma mutum ya zabi mutuwa a tafarkin Allah da a kashe shi domin Musulunci.

v    Mutuwa a kan gadon mutuwa ba komai ba ce illa mutuwa, amma shahada a tafarkin Allah abin alfahari ne da girmamawa ce ga mutum da kuma mutane.

v    “Jar Mutuwa” tafi “bakar mutuwa”.

v    Wace irin gafala da jahilci bayin duniya suke da ita, wadanda suke neman ma’anar shahada a shafukan littattafa na dabi’a, suke kuma neman siffofinsu a cikin wake da take da harzuka, suke kuma amfani da fasahar sakar zuci da liffan hankali domin gano su. Har abada ba za su taba fahimtan haka sai da kauna.

v    Shahidan juyin Musulunci mai girma, kamar shahidan farkon Musulunci suna da daukaka a wurin Allah kuma Allah Madaukakin Sarki da Shuwagabannin Musulunci na himmatuwa da su.

v    Kun ci nasara ne saboda kun rungumi shahada kuma wadanda ke tsoron mutuwa da shahada su ne masu karyewa.

v    Ashe shahada ba gado ba ce daga shugabanninmu wadanda suka dauki rayuwa tamkar imani da gwagwarmaya, wadanda kuma  suka kare Musulunci da jininsu, kuma suka gadar da ita ga al’ummarmu ma’abuciyar shahada.

v    Ina sanar wa jama’armu da miliyoyin mutanenmu cewa babu wani juyin da aka tabbatar da shi ba tare da neman shahada, sadaukarwa, kokari, wahala, shan wuya, tsadar kaya da rashinsu da matsa lamba ba.

v    Shahada a tafarkin Allah ba wata aba ce da za a kwatanta darajarta a ma’aunin dan Adam da abin duniya ba.

v    Shugabanmu shi ne wannan yaro[1] dan shekara 12 wanda karamar zuciyarsa tafi darurrukan harsunanmu da alkalummanmu, wanda ya rungumi nakiya ya fada da ita a karkashin tankar yaki ta abokan gaba ya rugurguza ta tare da kansa ya sha daga kogin shahada.

v    Farin cikina ga wadanda suka mayarwa Allah da abin da ya ba su (rayuwa), mu kuwa mu ne kashin bayansu da muka saura.

v    Ya saura gare mu da mu bayyana raunukanmu kuma mu nuna godiyarmu wa wadannan mayakan Musulunci wadanda suke neman shahada kuma ta hanyar jaruntaka suke kare kasarsu ta Musulunci da kuma tsarkakakken jininsu suka yada haske domin nuna wa al’ummomin da suke a cikin kangi hanya.

v    Son barka ga wadannan shahidai saboda abin da suka samu na jin dadin debe kewa da saduwa da Annabawa da Waliyai da kuma shahidan farkon Musulunci. Fiye da wannan kuma shi ne, barkansu da kaiwa ga ni’imar Allah wadda ita ce yardar Allah  mafi girma.

v    Ya ku shahidai; ku zama masu sanyin idaniya a kusaci da Allah, al’ummarku ba su yi sako-sako da cin nasarar da kuka samar ba.

v    Ku (shihidai) shaidu ne na hakika, wadanda ake tunawa da daukaka da jaruntaka kuma mafi dacewar bayi abin koyin bayin Allah masu tsarkin niyya, lalle kun tabbatar da mika wuyanku ga Allah Ta’ala da kuma bautarku gare shi ta hanyar ba da jininku da rayukanku.

v    Кasar da kowa a shirye yake domin sadaukar da rayuwarsa da yin shahada, da me kuma ake tsoratar da ita?

v    Hikima ita ce mutum ya yunkura don yin jihadi ba  tare da kwarmato na siyasa da shaidan ba, kuma ya sadaukar da kansa saboda manufar, ba wai saboda son rai ba wannan shi ne tafarkin addinin mutanen Allah.

v    Ina sanar da ku ya ku ‘yan ‘uwana muminai, zai fi mana kwarai idan miyagun Amirka da Rasha suka halaka mu kuma ta hanyar zub da jininmu mu koma ga Allah tare da mutunci, a kan mu dauki rayuwa ta jin dadi da holewa a karkashin tutar sojojin Gabas (Rasha) ko bakaken sojojin Yamma (Yammacin Turai).

v    Kada ku ji tsoro! Ku ne masu nasara InshaAllahu ko mun kashe ko kuma an kashe mu gaskiya tana tare da mu. Idan aka kashe mu zai kasance a tafarkin Allah, kuma idan muka kashe, wannan shi ma domin Allah ne, wannan kuwa ita ce nasara.

v    Sadaukarwa da fansa su ne makamashin juyi guda biyu kamar kuma yadda shahada da shirin ta larura ce a kowane juyi.

v    Mai jihadi a tafarkin Allah, ya wuce a kimanta kyawon aikinsa da ma’aunin alatun duniya.

v    Mu mazauna bayan kasa ko kuma halittun duniyar taurari yaya za mu iya sanin mene ne abin da aka tanadawa shahidai a gurin Ubangiji?

v    Duniya tare da dukkan kimarta da dadinta ta yi kadan kwarai ta zama wani bangare ko matsayi ga wadanda suka yi yaki a tafarkin Allah.

v    Idan ka kashe mu Insha Allahu, za mu shiga aljanna, kuma idan muka kashe, a nan ma zamu shiga aljanna.

v    Idan aka kashe ku, kuna daga cikin ‘yan aljanna haka kuma idan kuka kashe to kuna daga cikin ‘yan aljanna.

v    Idan muka kashe mun rabauta ko kuma aka kashe mu duk dai mun rabauta.

v    Matukar dai mun gaji wancan jinin, ma’abuta samun shahidai da matasan da suka saura, mu nutse cikin jinin shahidai, kada mu zauna haka kawai, mu yi iyakar kokarinmu mu ga mun kai gacin burin sadaukarwarsu.

v    Shahada kyauta ce daga Allah Madaukakin Sarki ga wadanda suka cancance ta.

v    Kuka ga shahidi yana rura wutan yunkuri ne.

v    Kuka wa shahidin da ya sadaukar da komansa a tafarkin Musulunci al’amari ne na siyasa kuma yana da tasiri mai yawa wurin ciyar da juyin gaba. Mu yi amfani da irin wadannan tarurruka.

v    Makabartar shahidai da jikkunansu da kuma jikkunan nakasassun yaki, harsuna ne masu ba da shaida game da girman matabbatar ruhinsu mai dorewa.

v    Jinin matasanmu ya yi galaba a kan bindigogi.

v    Ya ya za a yi mutanen da ke ganin karfinsu a jinin shahidanmu, ba za su yi ma mutum tasiri ba?

v    Hidima a Bonyad Shahid[2] (Mu’assasar Shahidai) ya fi kowane irin hidima.

v   Ina daukar shahada a tafarkin Allah kuma domin manufofi na addini a matsayin daukaka madawwamiya.

 


[1] . A nan Imam yana nufin wani saurayiin sojan sa kai (Basijii) mai suna Husaini Fahmidi ne. wannan saurayi ko da yake a lokacin yana da shekara 12 ne amma ya nuna jaruntaka kwarai da gaske lokacin yakin Iran da Iraki wanda aka shafe shekaru takwas ana yi sakamakon ziga kasar Iraki da kasashen Turai, musamman kasar Amirka, suka yi don ta fada wa Iran. Saboda jarunta da kwazon wannan yaro, kwamandojin yaki sukan barshi ya halarci fagen fama. Babban jaruntar da ya yi shi ne lokacin da ya sanya bama-bamai a jikinsa ya fada cikin rundunar abokan gaba don hana tankokin yakinsu kai hari, inda bama-baman suka fashe tankokin suka tarwatse shi kuma ya yi shahada. Wannan irin jarumta ya burge kowa, al’amarin da ya bude kofa ga sauran sojoji don su yi koyi. A sabili da haka ne ma Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanya hotonsa a jikin kudinta na riyal 100 da riyal 1000 don tunawa da kuma girmama wannan babban aiki da ya yi.

[2] . Ran 15/3/1980, Imam Khumaini (r.a) ya ba da umurnin kafa wata cibiya da sunan “Mu’assasar Shahidan Gwagwarmayar Musulunci” don kulawa da iyalan shahidai da kuma sojojin da suka sami nakasa. A cikin sakon da ya aika wa Hujjatul Islami wal Muslimin Mahdi Karrubi, Imam ya ba da umurnin cewa lallai ne a bada muhimmanci ga iyalan shahidai da sojojin da suka sami nakasa, don su sami ingantaccen ililmi, aikin yi da kuma kula da lafiyarsu. A halin yanzu wannan cibiya ta samar da ilimi da kuma ababan jin dadi ga wadannan iyalai da ‘ya’yayensu a duk fadin kasar Iran.