KADAN DAGA CIKIN KALAMAN IMAM RIDHA (A.S):
- Wanda ya dau lokaci da yin wahala wajen (rufa asirin) kansa da na iyalinsa kamar mutumin da ya yi Jihadi ne a tafarkin Allah.
- Duk lokacin da za ka kira sunan wani mutum, ka kira shi da girmamawa.
- Ka kiyaye tsabta, don tsabta na daga cikin halayen Annabawa.
- Mafi munin mutane shi ne, wanda kasantuwansa ba ta da wani amfani ga sauran mutane.
- Wanda ya cutar da musulmi, to ba ya daga cikinsu.
- Abokin mutum shi ne hikimarsa, kana jahilci kuma makiyinsa.