YANAYIN SIYASA DA KE KEWAYE DA HAIHUWAR MAHDI :
________________________
Tarihi dai ya nakalto mana irin
mawuyacin halin da Imam Hasan al-Askari (a.s) ya fuskanta daga wajen sarakunan
Abbasiyawa na lokacinsa, kamar yadda kuma muka ga irin halin dar-dar da rashin
zaman lafiya na siyasa, zamantakewa, tattalin arziki da tsaro da al’umma suke
fuskanta da kuma irin tsoron da mahukunta suke da shi cikin zukatansu dangane
da Ahlulbaiti (a.s).
A daidai wannan lokaci
na dar-dar da aka haifi Imam al-Mahdi (a.s) a cikinsa ne kuma aka kashe halifan
Abbasiyawa al-Mu’utaz a watan Rajab shekara ta 255 hijiriyya, wato kimanin
kwanaki goma sha takwas da haihuwar Imam al-Mahdi (a.s) kenan. Bayan kashe
Mu’utaz sai dansa al-Muhtadi ya dare karagar mulki da ci gaba da ayyukan da
iyaye da kakanninsa suka fara.
Bisa
wannan bayani, kamar yadda kuma ruwayoyi suka kawo, an haifi Imam al-Mahdi ne a
lokacin mulkin Muhammad al-Muhtadi, wanda mulkinsa ya ci gaba har na kimanin
shekara guda, kafin rikici ya shiga tsakaninsa da Kurdawan lokacin inda suka
kama shi da kuma kashe shi a
watan Rajab shekara ta 256 hijiriyya, sai kuma al-Mu’utamid ya dare karagar mulki.
Cikin
wannan lokaci dai Ahlulbaiti da mabiyansu sun fuskanci tsananin matsin lamba,
abin da ya haifar da yunkure-yunkuren mabiya Ahlulbaiti don fuskantar
mahukuntan.
Abul Faraj al-Isfahani ya ambaci
sunayen zuriyar Ali (a.s) da mabiya Ahlulbaitin da aka kashe ko kuma suka mutu
a gidajen yarin mahukuntan saboda azaba, kamar yadda kuma ya kawo bayani
kan yadda wannan
zalunci na Abbasiyawa ya yadu zuwa garuruwa daban-daban. Kamar yadda kuma al-Yakubi,
masanin tarihi, shi ma ya ruwaito wani sashi na irin zaluncin Abbasiyawan.
Abu ne dai da yake a
fili cewa halifofin Abbasiyawa sun riga da sun san cewa imamanci dai zai
kasance a zuriyar Husaini (a.s), don haka suka takurawa Imam al-Sadik (a.s) da
sauran imaman da suka zo bayansa, inda suka sanya wasunsu a gidajen yari tare
da mabiyansu da kuma kashe su, don kuwa suna da masaniyar cewa imamanci dai za
ta kai ga al-Mahdi al-Mau’ud dan Imam al-Askari (a.s).
Shaikh al-Mufid() ya bayyana cewa tsoron
irin ta’addancin da ake wa zuriyar Ali (a.s) da kuma masaniyar da Abbasiyawa
suke da shi na cewa karshen imamanci zai zo daga zuriyar Imam al-Askari (a.s)
da kuma kokarin da suke yi na kawo karshen imamancin, shi ne abin da ya sanya
Imam al-Askari (a.s) ya boye zance haihuwar dansa da kuma boye shi daga idon
mutane. Haka nan kuma duk wani mutumin da ma yake magana
kan Imam al-Mahdi ya
kan fuskanci azabobi da
takurawa daban daban. Ga abin da yake cewa:
“Mabiya Abu Muhammad
saboda fadin haka – wato fadin imamancin al-Mahdi – sukan fuskanci matsaloli da
suka hada da tsarewa, barazana, kaskantarwa…..()”.
Shaikh al-Mufid dai
ya rayu ne tsakanin shekara ta 338-413 hijiriyya, kusa da lokacin zamanin
wakilan Imam al-Mahdi na musamman, wato lokacin Ghaibat al-Sughra (karamar
buya) ta Imam al-Mahdi (a.s) wacce ta kare a shekara ta 329.
|