MATSAYA BAYAN SHAHADAR IMAM AL-ASKARI (A.S):

________________________

Imam al-Askari (a.s) ya yi shahada ne a shekara ta 260 hijiriyya, wannan shahada tasa kuwa ta haifar da damuwa da rudu mai girman gaske tsakanin ‘yan shi’a, ga tambayoyi daban-daban da suke ta fitowa, wasu na cewa, a’a shin Imam al-Askari ba shi da dan da zai gaje shi ne? Ko kuma shi kenan imamanci ya kawo karshe ne a bayansa don kuwa ba shi da da? An ta samun jawabai da amsoshi dai kala-kala.

 To sai dai kuma da yake wasu daga cikin na kurkusa da shi daman sun riga da sun san cewa yana da da, wato sun riga da sun sa zancen haihuwar Imam al-Mahdi (a.s), don haka sun amsa wa mutane wadannan tambayoyi nasu da kuma tabbatar musu da cewa yana da da, lamarin da ya kawar da wannan damuwa da suke da ita. A takaice an tabbatar da cewa Imam al-Mahdi dai shi ne Muhammad bn Hasan al-Askari wanda aka haifa cikin sirri a garin Samarra gabannin shahadar mahaifinsa da shekaru biyar.

 Haka dai Allah Madaukakin Sarki Ya so Ya tsawaita shekarun bayyanarsa, don ya cika duniya da adalci bayan ta cika da zalunci.