|
|
| |||
|
________________________
Littattafan ruwayoyi da hadisai sun ruwaito mana hadisai da
dama da Manzon Allah (s.a.w.a) ya ke sanar da al’ummar batun al-Mahdi (a.s) da
kuma cewa zai cika duniya da adalci da daidaito bayan ta cika da zalunci da
babakere. Don haka za mu iya fahimtar cewa imani da kasantuwan al-Mahdi (a.s) akida
ce ta Musulunci da dukkan musulmi suka yi imani da ita.
Sayyid
Abdullah Shabbar cikin littafinsa Hak al-Yakin ya nakalto cewa:
“Ku
sani cewa akwai busharar bayyanar Mahdi (a.s) cikin ingantattun hadisan shi’a
da sunna, kuma zai kasance cikin buya. Daga cikin wadanda suka ruwaito wadannan
hadisai a bangaren sunna kuwa har da, Bukhari, Muslim, Abu Dawud, Tirmizi da
mawallafin Jami al-Usuli da dai sauransu. Hakika an ruwaito sama da
hadisai dari da hamsin daga bangaren ‘yan sunna da suka magana
Har ila yau akwai wasu hadisan kuma da suka yi magana
Daga
cikin wadannan siffofi da ruwayoyi suka kawo akwai:
1-
Jaddadawa cewa shi Bakuraishe ne: “Ahmad da
Mawardi sun ruwaito cewa Manzon Allah (s.a.w.a) ya ce: “Ku yi bushara da
al-Mahdi, shi Bakuraishe ne, daga cikin zuriyata, zai bayyana a sabanin zaton
mutane, zai cika duniya da adalci da daidaito kamar yadda ta cika da zalunci da
babakere([2])”.
2-
Cewa Mahdi (a.s) zai kasance ne daga ‘ya’yan
Abdul Mutallib: Ibn Majah ya ruwaito daga Anas bn Malik cewa: “Na ji Manzon
Allah (s.a.w.a) yana cewa: “Mu ‘ya’yan Abdul Mutallib mu ne shuwagabannin
‘yan aljanna, ni da Hamza da Aliyu da Ja’afar da Hasan da Husaini da Mahdi([3])”.
3-
Cewa Mahdi daga Zuriyar Manzon Allah (s.) ya ke
kuma sunansa Muhammadu ne: Imam Ahmad bn Hambal yana cewa: “Fadhl bn Dalin ya
gaya mana, haka nan Yasin al-Ajli ya gaya mana daga Ibrahim bn Muhammadu bn
al-Hanafiyya, daga babansa Aliyu cewa: Manzon Allah (s.a.w.a) ya ce: “Mahdi
daga cikinmu Ahlulbaiti ya ke, Allah Zai yi gyara da shi (zai tayar da shi)
cikin dare guda([4])”.
Haka nan kuma ya ruwaito daga Sufyan cewa: “Duniya
ba za ta kare ba har sai wani mutum daga cikin mutanen gidana, wanda sunansa
irin sunana ne, ya mallake ta([5])”.
Ahmad bn Hambal da Abu Na’im sun fitar daga Abu
Sa’id al-Khudri cewa: Manzon Allah (s.a.w.a) ya ce:
“Duniya ba za ta kare
ba har sai wani mutum daga zuriyata ya mallake ta, ya kuma cika duniyar da
adalci kamar yadda aka cika ta da zalunci….”.
4-
Cewar Mahdi daga zuriyar
5-
Cewar halifofi guda sha biyu ne([7]):
Wasu ruwa-yoyin suna jaddada cewa Manzon Allah (s.a.w.a) ya yi nassi ne a
Wadannan hadisai dai- da ma wasunsu – da suke magana kan
cewa Mahdi zai kasance ne daga Ahlulbaiti, daga ‘ya’yan Fatima kana kuma
zuriyar Imam Husain (a.s), suna bayyana mana siffofin Imam al-Mahdi (a.s) ne,
musamman ma bisa la’akari da cewa wadannan hadisai ingantattu ne a bisa
mahangar shi’a da sunna.
Kamar
yadda kuma wadannan hadisai sun kai haddin da babu wanda yake shakku a kansu,
kai hatta ma dai dukkan malaman musulmi na da da na yanzu sun tafi akan samuwar
al-Mahdi al-Muntazar (a.s).
Sheikh
Abdul Muhsin al-Ibad([8]),
memba a kwamitin koyarwa na Jami’ar Musulunci ta birnin Madina al-Munawwara,
cikin wani jawabi da ya gabatar mai suna “Akidar Ahlussunna Kan al-Mahdi
al-Muntazar”, ya ambato sunayen sahabban da suka ruwaito hadisai kan Mahdi daga
Manzon Allah (s.a.w.a), inda ya kawo sunayen ashirin da shida daga cikin manyan
sahabbai, kamar yadda kuma ya ambato sunayen malamai talatin da takwas da suka
ambato wadannan hadisai cikin littattafansu, daga cikinsu kuwa akwai Abu Dawud
cikin Sunan dinsa, Tirmizi cikin Jami’i dinsa, Ibn Majah cikin Sunan dinsa,
Nisa'i cikin Sunan dinsa, Ahmad bn Hambal cikin Musnad dinsa, Ibn Habban cikin
sahihinsa, al-Hakim cikin Mustadrak dinsa da dai sauransu.
Haka nan Abdul’Aziz
bn Baz, shugaban jami’ar Musulunci ta Madina yana cewa: “Hakika al’amarin Mahdi
sanannen al’amari ne, akwai hadisai da dama (mutawatirai) da suka zo
([7]).
Jabir bn Samrata ya ce: ‘Wata rana ni da mahaifina mun je wajen Manzon Allah
(s.a.w.a) inda muka ji shi yana cewa: “Hakika wannan al’amari ba zai kare
ba har sai an samu halifofi guda goma sha biyu”, sai ya fadi wani abin
da ban ji ba, sai ya ce: sai na ce wa babana me ya ce ne: sai ya ce min: ya ce
ne dukkansu Kuraishawa ne. Dubi Sahih Muslim/ Kitab al-Imarah, hadisi na 3393. |
||||