WANE NE IMAM AL-MAHDI AL-MUNTAZAR (A.S):

________________________

An haifi al-Mahdi (a.s) ne a daren sha biyar ga watan Sha’aban shekara ta dari biyu da hamsin da biyar bayan hijira, mahaifinsa Imam al-Askari (a.s) ya yi shahada ne a lokacin da Imam al-Mahdi (a.s) yake da shekaru biyar a duniya, don haka an haifi Imam al-Mahdi (a.s) ne a lokacin halifancin al-Muhtadi al-Abbasi, wato lokacin fitina da zaman dar-dar.

Bayan haihuwarsa dai, mahaifinsa Imam al-Askari (a.s) ya kewaye shi da cikakkiyar kulawa saboda kare rayuwarsa da kuma cika alkawarin Ubangiji da kuma imamancin da shi ma ya gada daga iyaye da kakanninsa. Hakan kuwa ya biyo bayan bincikensa da azzaluman mahukuntan lokacin suke yi don kashe shi.

Shaikh al-Saduk ya ruwaito daga Ahmad bn Hasan bn Ishak al-Kummi cewa:

“Lokacin da aka haifi Imam al-Mahdi (a.s), shugabanmu Abu Muhammadu al-Hasan bn Ali (al-Askari) (a.s) ya aike wa kakana Ahmad bn Ishak da wasika da rubutunsa da kuma sa hannunsa (inda yake cewa): An haifi jaririn, ka kiyaye wannan batu, kada ka sanar da dukkan mutane, don ba za mu gaya wa kowa ba sai na kurkusa da masu imani wilayansa, mun sanar da kai ne don Allah Ya faranta maka rai kamar yadda Ya faranta mana. Wassalam([1])”.

Haka nan Shaikh al-Saduk ya ruwaito cewa Ahmad bn Ishak ya ce:

“Na ji Abu Muhammadu al-Hasan bn Ali al-Askari (a.s) yana cewa: Godiya ta tabbata ga Allah Wanda bai dauki raina ba har sai da na ga wanda zai gaje ni, mafi kamanci da Manzon Allah (s.a.w.a) a halitta da aiki tsakankanin mutane, Allah Madaukakin Sarki Zai kare shi a lokacin buyarsa, daga baya kuma ya bayyanar da shi don ya cika duniya da adalci da daidaito bayan ta cika da zalunci da babakere([2])”.

Yayin da yake magana kan shahadar Imam al-Askari (a.s) mahaifin Imam al-Mahdi (a.s), Shaikh al-Mufid yana cewa:

“Sai dansa, wanda ake jira don kafa daular gaskiya ya gaje shi, kafin haka dai ya boye haihuwa da kuma al’amarinsa saboda yanayin wancan lokacin, tsananin nemansa da shuwagabannin lokacin suke yi, bayanan da suka watsu dangane da shi tsakanin shi’a da kuma jiran dakon da suke masa, don haka ne mahaifinsa bai bayyanar da shi ga al’umma a lokacin rayuwarsa ba kamar yadda kuma ba su san shi ba bayan wafatinsa([3])”.

Dukkan ruwayoyi daga bangarorin shi’a da sunna sun tafi a kan cewa Mahdi (a.s):

1-      Daga zuriyar Fatima (a.s) yake.

2-      Daga zuriyar Husain (a.s).

Wannan dai abu ne da dukkan musulmi suka tabbatar da shi duk kuwa da sabanin mazhaba da ra’ayuyyukan da suke da shi, to sai dai kuma kari kan haka, mabiya Ahlulbaiti (a.s) suna ganin cewa Mahdi (a.s) shi ne:

1-      Muhammadu bn al-Hasan al-Askari (a.s).

2-      Kuma shekarunsa biyar ne lokacin wafatin mahaifinsa.

3-      Kuma, cikin ikon Allah, ya buya daga idanuwan mutane, kuma wannan buya tasa tana da marhaloli guda biyu:

a). Marhalar Karamar Buya: A wannan lokaci ya kan sadu da mutane ne ta hanyoyin wakilansa guda hudu.

b). Marhalar Babbar Buya: A wannan lokaci saduwarsa da mutane ta hanyar wadannan wakilai ta kawo karshe bayan ya sanar da su haka, don haka sai ya koma da su wajen malamai (al-Fukaha’) har lokacin da zai samu yanayin da ya dace don bayyanarsa da kuma gyaran al’umma da tsayar da daular adalci ta Ubangiji da aka jima ana jiranta.

Hakika Manzon Allah (s.a.w.a) a ruwayoyi da dama ya bayyana matsayin Ahlulbaiti (a.s) da kuma wajibcin binsu da riko da tafarkinsu, daga cikinsu kuwa har da fadinsa (s.a.w.a) cewa: Matsayin Ahlulbaitina a cikinku kamar matsayin Jirgin (Annabi) Nuhu ne, wanda ya hau shi ya tsira, wanda kuwa ya saba masa ya halaka”.

Da kuma fadinsa (s.a.w.a) cewa: Lalle ni na bar muku wasu nauyaya guda biyu: Littafin Allah da Zuriyata Ahlulbaiti, matukar kuka yi riko da su to ba za ku taba bata ba([4])”.

Har ila yau kuma a cikin wadannan ruwayoyi akwai ishara ga ci gaban kasantuwan Ahlulbaiti (a.s) a gefen Alkur’ani mai girma, wato Alkur’ani da Ahlulbaiti ba za su taba rabuwa ba. Bugu da kari kuma akwai wasu hadisan daga Manzon Allah (s.a.w.a) da suke magana kan cewa halifofi dai guda goma sha biyu ne kuma Mahdi daga zuriyar Husaini (a.s) yake, kamar yadda kuma akwai ruwayoyi daga Imamai (a.s) da suke nuni da cewa shi ne na tara daga cikin ‘ya’yan Husaini, da dai sauransu da suke bayyana mana cewa Imam al-Mahdi dai shi ne Muhammadu bn al-Hasan al-Askari (a.s).

Ala kulli halin dai, dukkan musulmi dai sun tafi a kan imani da Mahdi (a.s) da kuma cewa shi ne mai gyara da kuma ‘yantar da wannan al’umma daga zaluncin da take ciki.



([1]). Bihar al-Anwar na Majlisi, juzu’i na 51, shafi na 16.

([2]). Kamar na sama, shafi na 161.

([3]). Al-Irshad na Shaikh al-Mufid, shafi na 345.

([4]). Ihya’ al-Mayyit bi zikri Fadha’il Ahlulbaiti na al-Suyuti.