IMAM AL-MAHDI AL-MUNTAZAR (A.S):

________________________

Rikici tsakanin alheri da sharri a doron kasa dai ya faro ne tun daga farko-farkon wannan duniya tamu, kuma wannan gasa da rikici zai ci gaba da samuwa tsakanin tafarkoki guda biyu; tafarkin shiriya da tafarkin bata; tafarkin Annabawa da tafarkin jahilai dawagitai.

Hakika sakon Musulunci ya samu nasara ta hannun Manzon Allah (s.a.w.a) kuma haka wannan tafarki ya ci gaba har ya gina tafarkin tauhidi, ya ciyar da dan’Adam gaba bisa asasin ilmi da imani, ya samu haskakuwa da wannan haske kana kuma ya shiryu da wannan shiriya madaukakiya.

To sai dai kuma daga baya wannan tafarki ya fara yin rauni, lokacin da wasu akidu da wayewa na jahiliyya suka fara kunno kai, aka fara samun koma baya a wayewa ta Musulunci, aka hana dan’Adam rayuwa karkashin inuwar imani, gaskiya, adalci da zaman lafiya. A bangare guda kuma zalunci ya ci gaba da yaduwa a fadin duniya, al’adun jahiliyya suka fara samun gindin zama, har muminai suka fara yanke kauna, ba don dai suna tunanin alkawarin Ubangiji ba na cewa zai taimaki addininSa da kuma tabbatar da adalci da kawo karshen zalunci da fasadi ba ta hannu wani mai kawo gyara, wanda zai tsayar da sunnar Annabawa da kuma gina rayuwa bisa asasin Alkur’ani da Sunna Manzon Allah (s.a.w.a), wannan mutumi kuwa shi ne ‘Mahdi (Mai Shiryarwar) wannan al’umma’ kamar yadda Manzon Allah (s.a.w.a) ya ambace shi cikin ruwayoyi daban-daban. Babu shakka hakan kuwa alkawarin Ubangiji ne tabbatacce cikin Alkur’ani da sauran Saukakkun litattafa.

Wannan Mai kawo gyara dai da dawo da kaunar da muminai suke da shi na kawo karshen jahiliyya, zai cika duniya da adalci da daidaituwa bayan ta cika da zalunci da babakere.