Shahadar Imam Al-Askari (a.s):

________________________

Imam Hasan al-Askari (a.s) ya yi zamani ne da sarakunan Abbasiyawa irin su Mu’utaz, Muhtadi da Mu’utamid, inda ya fuskanci matsin lamba da takurawa mai girman gaske daga wajen wadannan sarakuna (halifofi) guda uku, kamar yadda kuma suka sha kama shi da kuma tsare shi.

Sarki na karshe da Imam al-Askari (a.s) ya rayu da shi shi ne Mu’utamid wanda ya kasance mai son wasa, wargi, kide-kide da shaye-shaye, lamarin da ya sanya al’umma suka ki shi ki na gaske([1]).

A wannan lokaci kuwa Imam (a.s) ya fuskanci matsin lamba mai tsananin gaske daga Mu’utamid da kuma sanya idanuwa kan dukkan ayyukan da ya ke gudanarwa da kuma koran duk wani wanda ya ke son ganawa da shi([2]).

Ba komai ya sa shi da sauran Abbasiyawa daukan wannan kakkausar mataki ba face dai irin gaba da hassadan da suke yi kan matsayin da Imam (a.s) yake da shi a zukatan al’umma da kuma tsoron da suke ciki na haihuwar dansa Imam al-Mahdi (a.s), wanda tuni daman sun riga da sun san cewa zai kasance ne daga tsatson([3]) Imam al-Askari (a.s). Imam al-Askari (a.s) ya yi nuni da wannan batu cikin wata wasikarsa inda ya ce:

Suna tunanin kashe ni don su kawo karshen wannan zuriya, lalle Allah Ya karyata wannan zance nasu, godiya ta tabbata ga Allah([4])”.

Hassada da gaban Mu’utamid dangane da irin kaunar da al’umma suke nunawa Imam (a.s) sai dada karuwa suke yi, alhali a kullum al’umma sai kara tsanansa suke yi, don haka sai ya yanke shawarar kama Imam da kuma kashe shi.

Hakan kuwa ya faru, don ya sanya masa guba mai tsananin gaske cikin abincinsa inda ya yi kwanaki yana kwance cikin halin rashin lafiya mai tsanani sai dai kuma ya yi hakuri da kuma neman kusanci da Allah Madaukakin Sarki([5]). Inda ya yi shahada a shekara ta 260 hijiriyya alhali yana dan shekaru ashirin da takwas.

Amincin Allah ya tabbata a gare shi, ranar da aka haife shi, ranar da ya yi shahada da ranar da za a tashe shi a matsayin wanda aka zalunta.



([1]). Hayat al-Imam al-Askari na Bakir Sharif al-Karshi, shafi na 255, yana mai nakaltowa daga Tarikh al-Khulafa’, shafi na 363.

([2]). Kamar na sama.

([3]). Bisa hadisan da suka zo daga Manzon Allah (s.a.w.a) kan wannan batu, kamar yadda za mu kawo su nan gaba.

([4]). Hayat al-Imam al-Askari na Bakir Sharif al-Karshi, shafi na 255, yana mai nakaltowa daga Kifayat al-Athar  na al-Khazzar al-Kummi al-Razi, daga cikin malaman karni na hudu.

([5]). Kamar na sama, shafi na 267, ya nakalto daga Muhaj al-Da’awat, shafi na 247.