|
|
| |||
|
________________________ Mahukuntan Abbasiyawa sun dau matakan takurawa Imam al-Askari (a.s) ta hanyar sanya ido kansa da ayyukan da yake gudanarwa, da nufin kawo karshen ayyukansa da kuma hana shi ba da gudammawarsa ta jagoranci da shiryar da al’umma…..
Don haka Imam al-Askari (a.s) ya zabi tafarkin gudanar
da ayyukansa a asirce ba tare da ‘yan leken asirin Abbasiyawa sun gane ba, ta
hanyar zaban wasu wakilai da za su gudanar da ayyuka da yawunsa da dai sauran
hanyoyin da ya bi da tarihi ya tabbatar mana da su. 1- Abu Hashim al-Ja’afari ya ruwaito daga Dawud bn al-Aswad da Kaddam, daya daga cikin masu hidima wa Imam (a.s) cewa:
“Wata rana shugabana Abu Muhammadu (Imam
al-Askari) ya kira ni ya bani wani katako (ice) kamar kafar kofa mai tsawo, ya
ce min: Ka kai wannan katakon ga al-Amri.
Sai na karba na ci gaba da tafiya, a kan hanyata
sai na ci karo da wani mai bayin ruwa tare da alfadarinsa, sai wannan alfadari
ya tsare min hanyar wucewa, sai mai alfadarin ya ce min in masa tsawa don koro
masa shi, maimakon haka sai na dauki wannan katako na bugi alfadarin nan da
shi, sai katakon ya tsage. Ko da na dubi katakon sai na ga takardu a ciki, nan
take sai na tattara wannan katako da rike shi. Ganin haka sai wannan mutum ya
kira ni yana ta zagina.
Koda na dawo sai Isa mai hidima ya tarbe ni
bakin kofa, ya ce: shugabanmu yana ce maka: Me ya sa ka bugi alfadarin nan (da
katakon) har ka karya shi.
Sai na ce masa: Ya shugabana! Ban san abin da ke
cikinsa ba ne.
Sai ya ce: To amma me ya sa ka nemi yin
musu kan abin da za ka nemi uzuri bayan ka aikata shi, ina gargadinka da ka da
ka sake aikata hakan, idan ka ji wani yana zaginmu ka ci gaba da abin da aka
umarce ka da aikatawa, kuma ina gargadinka da kada ka tanka wa wani wanda ya
zage mu, ko kuma ma ka bayyana masa kai wane ne. Muna kasa ce da zalunci ya yi
wa kanta, ka ci gaba da tafiyarka, don kuwa labarinka da halin da kake ciki duk
yakan iso gare mu, lalle ya kamata ka san haka([1])”.
2- Daga Muhammadu bn Abdul’aziz al-Balkhi, yace:
“Wata rana da safe na zauna a bakin hanya, sai
ga Abu Muhammadu (Imam al-Askari) (a.s) ya fito daga gidansa……, sai na ce a
cikin zuciyata: Idan na ce Ya ku jama’a, wannan hujjar Allah ne a kanku don
haka ku san shi, za a kashe ni?
Lokacin da ya matso kusa da ni, sai ya yi ishara
da yatsarsa manuniya: da in yi shiru.
A wannan daren sai na ganshi yana ce min: “Abin
dai ko boyewa ne ko kuma kisa, don haka ka ji tsoron Allah a
|
||||