|
|
| |||
|
________________________
Tarihi da
hadisai cike suke da bayanai
1-
Muhammadu al-Shakiri yana cewa: “Imam (a.s) ya
kasance ya
2-
Al-Kulayni ya nakalto wata ruwaya da take magana
kan ibada Imam al-Askari (a.s), zuhudunsa da kuma amfani da lokacin da yake
tsare a kurkuku wajen zikiri, ibada da komawa ga Allah Madaukakin Sarki, abin
da ya yi tasiri ga mutanen da aka ba su aikin kulawa da kuma azabtar da shi,
yana cewa:
“Wata rana Abbasiyawa sun shiga wajen Saleh bn
Wasif, lokacin da aka tsare Abu Muhammad (Imam al-Askari), suka ce masa: Ka
takura masa kada ka bar shi ya walwala….”.
Sai Saleh ya ce musu: ‘Me zan yi masa, bayan da
na wakilta wasu mutane biyu masu tsananin kaushin zuciya (don kula da shi),
amma sai suka koma mutane masu ibada, salla da azumi’.
Sai ya yi umarni da azo da wadannan mutane biyu,
ya ce musu: Kaiconku! Me kuka sani dangane da wannan mutumin?
Sai suka ce masa: Me za mu ce
Lokacin da Abbasiyawan suka ji haka, sai suka
watse cikin fushi([2])”.
Irin lalacewar dabi'u,
siyasa, yadda ake gudanar da al’amurra, zaluncin da ya yi yawa, fasadi da wasa
da dukiyar al’umma da dai sauran nau’oi na zalunci da ta’addanci a kan al’umma
da mahukunta suke yi, sannan a bangare guda kuma ga talauci da mummunan yanayin
da al’umma suke ciki sakamakon ayyukan mahukunta, suna daga cikin abubuwan da
suka sanya Imam al-Askari (a.s) ya nuna rashin amincewarsa da kuma wayar da kan
al’umma kan irin wannan yanayi da ake ciki.
Wannan matsaya da Imam din ya dauka ta sanya
mahukuntan lokacinsa, wato gwamnatin Mu’utaz, Al-Mahdi da ta al-Mu’utamid suka
shirya don fuskantarsa da kuma takura masa rayuwa ta hanyoyi daban-daban. |
||||