Halayen Imam Hasan bn Ali Al-Askari (a.s):

________________________

Imam al-Askari (a.s), kamar sauran iyaye da kakanninsa, ya kasance wata alama ce da ba ta buya, Imami wanda babu wanda ya jahilce shi, ya kasance malamin malamai, abin koyin masu ibada, jagoran addini da siyasa, wanda ake nuni shi (da yatsa) kana kuma zukata suke komawa gare shi da so da kauna.

Duk kuwa da ta’addancin Abbasiyawa, adawa ta siyasa da Ahlulbaiti (a.s), azabtarwa da takuran da mahukunta suke musu da mabiyansu da kuma sanya su a gidajen yari, duk da irin wadannan abubuwa, to amma halifofin lokacinsa sun gaza wajen boye matsayi da hakikaninsa ko kuma lalata matsayi da gudummawarsa ta ilmi da siyasa bugu da kari kan matsayinsa na zamantakewa. Hakika ya samu daukaka da fifiko sama da masu adawa da shi a zukatan al’umma.

Ahmad bn Abdullah bn Khakan, wanda yana daga cikin masu adawa da Imam al-Askari (a.s) ya nakalto mana irin matsayi da daukakan da Imam din yake da shi na siyasa da zamantakewa.

Ibn Shahr Ashub yana cewa:

“Husain bn Muhammadu al-Ash’ari yana cewa, Muhammadu bn Aliyu yana cewa: An ambato sunan Ahlulbaiti a wajen Ahmad bn Abdullah bn Khakan – wanda ya kasance nabisi ne (mai adawa da Ahlulbaiti) – a garin Kum(đ), sai ya ce:

Ban taba gani daga gare su kamar abin da na gani a wajen Hasan bn Ali bn Muhammadu bn Ridha ba, wata rana ya zo ya shiga wajen babana(đđ), ya ce: ‘Abu Muhammadu bn al-Ridha ne yake sallama, sai ya ba shi izini ya kuma tarbe shi da zaunar da shi a wajen sallarsa, ya ci gaba da yi masa magana da amfanar da shi har lokacin da ya mike zai tafi, ya raka shi. Daga nan sai na tambayi babana kan wannan mutumin, sai ya ce:

“Ya dana! Wancan shi ne shugaban Rafidhawa(đđđ), da za a kwace halifanci daga wajen Abbasiyawa, to da babu wani daga cikin Bani Hashim da ya cancanci wanda matsayi kamarsa, saboda falalarsa, kamewa, azumi, salla, gudun duniya da dai sauran halayensa.

Na kasance na kan yawaita tambaya a kansa, amma a koda yaushe sukan daukaka shi da ambaton karamominsa.

Sai ya ce: Ban taba ganin mai yawan ilmi, mai yawan hakuri, mai yawan kamewa kamar Hasan al-Askari ba([1])”.

Irin wannan matsayi na Imam al-Askari (a.s) da matsayarsa ta siyasa kan ja’irar gwamnatin Abbasiyawa ta wancan lokacin da kuma matsayinsa na jagoran ‘yan adawa ta siyasa ya sanya mahukuntan suka sanya masa takunkumi da daurin talala da kuma tilasta masa zuwa fadan sarki a ranakun litinin da alhamis na kowani sati.

Yayin da yake bayani kan wannan lamari, daya daga cikin sahabban Imam al-Askari (a.s) na cewa:

“Wata rana mun taru a al-Askar (Samarra), don kallon hawan Abu Muhammadu (Imam al-Askari), sai ga umarni daga gare shi cewa: Ku sani kada wani daga cikinku ya gaishe ni, kuma ka da wani ya nuna ni da yatsa, ko kuma ya sunkuya min don kuwa ba ku da tsaro wa kawukanku([2])”.

Muna iya ganin matsayi da daukakan da Imam (a.s) yake da su a zukatan al’umma idan muka yi dubi cikin wannan bayani da littattafan tarihi suka ruwaito mana kan halin da mutane suka shiga ranar shahadarsa:

“Lokacin da labarin wafatinsa ya watsu garin Samarra ya shiga wani irin hali na damuwa, aka rufe shaguna, inda Bani Hasim, shuwagabanni, malamai, alkalai kai da sauran al’umma gari duk suka nufi wajen jana’izarsa, a wannan ranar dai garin Samarra ya cika makil da kuma tashin hankali kai ka ce tashin kiyama ne….([3])”.



(đ). Kum: Wani gari ne daga cikin garuruwan kasar Iran mai dimbin tarihi da tsarkaka, a garin ne kabarin Fatima al-Ma’asumah ‘yar Imam Musa al-Kazim (a.s) yake kana kuma a wannan gari ne a ke da Makarantun Hawzah na ilmi Ahlulbaiti inda manyan malamai suke ba da darussa.

(đđ). Babansa Abdullah bn Khakan ya kasance daga cikin ministocin sarki Mu’utamad al-Abbasi kana kuma na kurkusa da shi.

(đđđ). Shugaban Rafidhawa: Na nufin shugaban ‘yan shi’an Ahlulbaiti (a.s), da wannan sunan ake kiransu a wancan lokacin.

([1]). Manakib Al Abi Talib na Ibn Shahr Ashub, juzu’i na 4, shafi na 423.

([2]). Bihar al-Anwar na Majlisi, juzu’i na 50, shafi na 269.

([3]). Al-Irshad na Shaikh al-Mufid, shafi na 340.